in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Beijing ta fara tantance adadin masu gurbata muhalli
2018-03-08 09:25:14 cri
A jiya Laraba gwamnatin Beijing ta kaddamar da shirin tantance adadin masu gurbata muhalli, a matsayin wani shiri da zai taimaka wajen kiyaye muhalli, da kuma aiwatar da kashi na biyu na shirin kasar Sin na gano hanyoyin dake gurbata muhalli.

Binciken, wanda ake burin cimma alkaluman da aka yi kiyasa tun daga shekarar 2017, zai taimaka wajen tantance cikakkun alkaluman manyan hanyoyin dake haifar da gurbatar muhalli, wanda ya kunshi adadin masu gurbata muhalli daga bangaren masana'antu, da aikin gona, da bangaren wuraren zama, da kuma yadda za'a tunkari matsalar ta magance gurbatar muhalli.

Sakamakon da za'a samu daga binciken zai taimaka wajen kara sanya ido kan masu gurbata muhallin da kuma yadda za'a tabbatar da ingancin muhalli. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China