in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin tana habaka hadin gwiwar ayyukan gona a tsakaninta da Afirka ba tare da wani sharadi ba
2018-03-07 13:41:44 cri
Ministan harkokin gona na kasar Sin Han Changfu ya bayyana a yau cewa, kasar Sin tana yin hadin gwiwa da kasashen Afirka a fannin ayyukan gona da taimakawa kasashen Afirka a fannin samar da isassun abinci ba tare da gindaya wani sharadi ba.

Yana mai cewa, an kafa cibiyoyin raya fasahohin ayyukan gona a kasashen Afirka guda 14, inda Sin ta tura masana da dama zuwa kasashen. Haka kuma, Sin ta gayyaci masana da jami'an hukumomin ayyukan gona na kasashen Afirka zuwa nan kasar Sin domin kara samun kwarewa kan wasu fasahohin zamani.

Ya kara da cewa, kasar Sin ta kuma samar da taimako ga wasu kasashen Afirka a fannonin na'urorin ayyukan gona na zamani da maganin kashe kwari masu barnata amfanin gona da dai sauransu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China