in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ba kasa ce da ta fi baiwa kasashen Afirka basusuka ba
2018-03-06 20:31:34 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau Talata cewa, a halin yanzu ba kasar Sin ba ce kasar da ta fi baiwa kasashen Afirka basusuka, kasashen Afirka sun dade suna karbar basusuka, ba wadannan shekaru biyu kawai ba. Geng Shuang ya bayyana hakan yayin da yake mayar da martini game da zargin da wani jami'in ma'aikatar harkokin wajen kasar Amurka kan hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka,

Ya ce, ko wace kasa tana bukatar kudade da farko yayin da take kokarin raya tattalin arziki da masana'antunta. Idan babu kudi, zai yi wuya ga kasashen Afirka su cimma burin raya masana'antu da zamanintar da kasashensu.

Geng Shuang ya jaddada cewa, kasar Sin ta dora muhimmanci sosai kan batun basusukan da kasashen Afirka suke karba. Sin na daukar ra'ayin samun bunkasuwa tare, da gina muhimman kayayyakin more rayuwa da su taimaka wajen raya sana'o'in kasashen Afirka, da cin gajiyar tattalin arziki da zamantakewar al'umma, da inganta karfin kasashen Afirka na samun bunkasuwa mai dorewa da kansu, da taimakawa kasashen Afirka wajen magance karuwar basusukan da ake binsu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China