in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijar: Kasancewar masu neman mafaka na damuwar al'ummar Agadez
2018-03-07 09:08:41 cri
Tun lokacin bude reshen cibiyar hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD cewa da HCR, suna da yawa 'yan gudun hijirar kasashen Sudan, Pakistan da Bangladesh dake kwarara zuwa birnin Agadez. Wadannan bakin haure dake ficewa daga kasar Libiya suna isowa Agadez domin fatan samun taimakon HCR da kuma neman samun mafaka kafin su wuce zuwa kasashen Turai bisa ka'ida.

Tuni ma bisa wannan tsari na hijira mai ruwa biyu, tare da aikin taimakawa 'yan gudun hijira da reshen HCR ya kaddamar, an kididdige 'yan gudun hijira fiye da dubu daya dake neman mafaka da suka fito daga kasashen Nijeriya, Afrika ta Tsakiya, Sudan da ma kuma 'yan kasashen Pakistan da Bangladesh dake isa birnin Agadez a cewar wasu majiyoyin na wannan hukumar kasa da kasa. Wakilinmu dake kasar Jamhuriyar Nijer Adam Maman ya aiko mana labarin. (Ada Maman)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China