in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rikicin manoma da makiyaya a Nijar ya yi ajalin mutum 34
2017-11-22 10:13:48 cri
Wani rikici tsakanin manoma da makiyaya da ya barke a wani kauye dake jihar Maradin Jamhuriyar Nijar daga daren ranar Litinin zuwa wayewar safiyar ranar Talata, ya yi ajalin wasu mutum 34.

Rahotanni daga Nijar din na cewa, rikicin ya barke ne, a lokacin da wasu manoman wurin suka yi korafin cewa makiyaya suna barin shanunsu su shiga gonakinsu, abun da ya sa manoman suka yi ramuwar gayya. Kawo yanzu rikicin ya hallaka a kalla mutane 34, kana, an kone gidaje sama da goma kurmus.

Rahotannin sun kara da cewa, an dade ana zaman doya da manja tsakanin manoma da makiyaya a yankunan kudancin Nijar, kana ana yawan samun hargitsi tsakaninsu sakamakon shiga gonakin manoma da dabbobin makiyaya suke yi.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China