in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a bude taron shekara shekara na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin
2018-03-04 14:25:16 cri
Za a bude zaman taron farko na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin karo na 13 a babban dakin taron jama'ar kasar Sin dake nan birnin Beijing a gobe Litinin ranar 5 ga wannan wata. An ce, za a gudanar da taron daga ranar 5 zuwa 20 ga watan Maris a birnin Beijing, wato ke nan za'a shafe kwanaki 15 da rabi, don haka, taron na wannan shekara zai kasance mafi tsawon lokaci kana mafi yawan batutuwan da za a tattauna a cikin shekarun da suka gabata.

A gun taron manema labaru da aka gudanar game da taron a yau Lahadi, sabon kakakin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin a wannan karo Zhang Yesui ya bayyana cewa, akwai ayyuka 10 da za a gudanar a taron a wannan karo, ciki har da sauraron rahoton ayyukan gwamnatin kasar, da duba rahoto game da yadda ake aiwatar da shirye-shiryen kasar, da shirin kasafin kudin kasar, da duba daftarin gyaran kundin tsarin mulkin kasar, da dokokin sa ido kan harkokin kasar, da rahoton ayyukan zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar, da rahoton ayyukan kotun koli ta kasar, da hukumar koli gabatar da kararraki ta kasar, da shirin yin kwaskwarima kan hukumomin majalisar gudanarwar kasar, da zaben jami'an hukumomin gwamnatin kasar da dai sauransu.

An ce, za a kira tarurukan manema labaru 14 a yayin taron, tarukan da za su shafi manyan batutuwan da ke jawo hankalin al'umma, ciki har da gyara kundin tsarin mulki da kafa dokoki, da harkokin sa ido. A safiyar ranar 20 ga wannan wata ake saran rufe taron, sabon firaministan kasar zai gana da 'yan jarida na gida da na waje tare da amsa tambayoyinsu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China