in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu shugabannin jam'iyyun siyasa da kwararru da masana na kasashen gabashin Afirka sun yaba da tafarkin da kasar Sin take bi wajen neman ci gaba
2018-03-03 14:19:15 cri
Gabannin zaman taron farko na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin karo na 13 wanda za'a yi a birnin Beijing, wasu shugabannin jam'iyyu masu mulki gami da masana da kwararru daga kasashen gabashin Afirka, ciki har da Kenya da Tanzaniya da kuma Uganda sun jinjinawa gwamnatin kasar Sin saboda tsarinta na gurguzu mai sigar musamman da nasarorin da ta samu wajen neman ci gaba. Sun bayyana cewa, tunanin gurgurzu mai sigar musamman ta kasar Sin a sabon zamani gami da tsarin majalisar wakilan jama'ar kasar, su ne tabbaci mai inganci ga kasar Sin wajen neman ci gaba.

Babban sakataren jam'iyya mai mulkin Kenya wato jam'iyyar Jubilee, Raphael Tuju ya jaddada cewa, ci gaban da kasar Sin ta samu ya shaida cewa, kar a kwaikwayi tsarin siyasa da tsarin demokuradiyya irin na kasashen yammacin duniya daga dukkan fannoni. Kenya na bukatar koyon nasarorin da gwamnatin kasar Sin ta samu, a fannonin da suka shafi alaka tsakanin kabilu da raya kasa da jam'iyyun siyasa da kuma lalibo wata hanyar da ta fi dacewa wajen neman bunkasa.

Shi ma a nasa bangaren, shehun malami Otiato Wafula daga sashin nazarin ilimin siyasa na jami'ar Kenyatta dake kasar Kenya ya ce duk da cewa yanayin da ake ciki a kasar Sin da na Afirka ba daya ba ne, amma suna da muhimman ayyuka kusan irin daya, wadanda suka hada da habaka tattalin arziki da kyautata zaman rayuwar al'umma da kuma kawar da talauci. Malamin ya ce, tsarin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ya samar da wata muhimmiyar turba da jama'ar kasar za su bi don neman ci gaba a fadin kasar.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China