in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyyar dake mulkin Najeriya za ta gudanar da muhimmin taro gabanin zabukan 2019
2018-02-27 09:50:02 cri
Ana sa ran shugaban Najeriya Muhammadu Buhari zai jagoranci taron kwamitin zartaswa na jam'iyyar APC mai mulkin kasar gabanin babban taron zaben shugabannin jam'iyyar wanda za'a gudanar a Abuja, babban birnin kasar.

Taron dai zai tattauna muhimman batutuwan da suka shafi kasar, da rikicin cikin gida da ya dabaibaye jam'iyyar, da kuma cimma matsaya game da takamammen lokacin da za'a gudanar da babban taron jam'iyyar na kasa.

Da ma dai shugaba Buhari ya nada Bola Tinubu, tsohon gwamnan jahar Legas, domin ya jagoranci kwamitin tuntuba da sasanta rikice-rikicen da ya addabi jam'iyyar ta APC mai mulkin kasar.

Ayyukan da aka damkawa Tinubu, sun hada da warware rashin fahimtar juna da takun-saka a tsakanin mambobin jam'iyyar, da masu rike da mukaman siyasa a wasu jihohin kasar.

Shi dai babban taron jam'iyya, ya kasance a matsayin wani dandali ne dake baiwa jam'iyya damar yin gyare gyare kan manufofinta da tsare-tsarenta, da kuma zabar jagorori da yin sauye-sauye a tsarin shugabancin jam'iyyar da yin gyaran fuska ga kundin tsarin mulkin jam'iyyar da dai sauransu.

A watan Fabrairun shekarar 2019 ne za'a gudanar da manyan zabuka a Najeriya. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China