Onyema Nwachukwu, mai magana da da yawun rundunar sojin dake Maiduguri, babban birnin jahar Borno, a arewa maso gabashin kasar ya bayyana cewa, an harbe mayakan na Boko Haram ne har lahira a wata maboyarsu dake Parisu, a kusa da dajin Sambisa a Juma'ar data gabata.
Kakakin rundunar sojin ya ce, sojojin sun ceto fararen hula 3 wadanda 'yan Boko Haram din suka yi garkuwa da su a lokacin samamen da sojojin suka kaddamar a yankin.
A cewar Nwachukwu, da ma dakarun sojin Najeriyar suna hakon mayakan na Boko Haram ne tun a ranar Alhamis din da ta gabata.
Boko Haram ta fara kaddamar da hare haren ta'addanci ne tun a shekarar 2009, a fafutukar da take na kafa daular Musulunci a shiyyar arewa maso gabashin kasar, inda ta yi sanadiyyar kashe rayukan jama'a sama da 20,000, ta kuma raba miliyoyin mutane da muhallansu.(Ahmad Fagam)