Lai Mohammed, ministan yada labarai da raya al'adu na Najeriya ya ce, gwamnati ta umarci jami'an 'yan sanda da na kare fararen hula a jahar Yoben da su hanzarta tura jami'ansu zuwa dukkan makarantun jihar domin tabbatar da tsaro. Ya ce gwamnati ta dauki dukkan matakan da suka dace domin ceto 'yan matan da aka sace domin dawo da su zuwa ga iyayensu lami lafiya, ya kara da cewa, hukumomin tsaron kasar na ci gaba da daukar matakan gano inda mata 'yan makarantar suke. (Ahmad Fagam)