in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Najeriya na ci gaba da tsananta binciken yara 'yan makarantar mata 110 da aka sace
2018-02-26 09:51:36 cri
Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadi cewa, tuni ta baza jami'an sojin sama da kayan aiki, da suka hada da masu tattara bayanan sirri, da masu bincike da daukar bayanai ta sama, a kokarin da take na binciko yara mata 'yan makaranta da suka bace a shiyyar arewa maso gabashin kasar.

Kakakin sojin saman Najeriya Olatokunbo Adesanya, ya ce, dakarun sojin saman na ci gaba da aikin binciko yaran ba dare ba rana.

Ana zargin kungiyar 'yan ta'adda na Boko Haram ne suka yi garkuwa da yaran, bayan wani harin da suka kaddamar a makarantar sakandaren 'yan mata ta kimiyya da fasaha dake Dapchi a jahar Yobe, shiyyar arewa maso gabashin kasar a ranar Litinin din da ta gabata.

Gwamnatin Najeriya ta sanar a ranar Lahadi cewa, ba'a ga yara mata 'yan makarantar kimanin 110 ba tun bayan harin da mayakan suka kaddamar.

Adesanya ya ce, a bayyane take dakarun sojojin na ci gaba da kara kokari tare da hadin gwiwar sauran jami'an tsaro domin binciko 'yan matan.

Kakakin sojojin ya bayyana cewa, gwamnatin kasar ta daura aniyar kubutar da dukkan yaran 'yan makarantar da suka bace. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China