in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta kafa sabuwar rundunar soji don shawo kan matsalar kalubalen tsaro
2018-02-23 09:41:30 cri
Babban hafsan sojojin Najeriya Lt.-Gen. Tukur Buratai ya kaddamar da wata sabuwar runduna ta 17 ta sojojin kasa a jahar Katsina dake shiyyar arewa maso yammacin kasar da nufin tunkarar kalubalolin tsaro a shiyyar.

Babban jami'in sojin ya ce makasudin kafa wannan rundunar soji shi ne, domin daukar matakan shawo kan dunbun kalubalolin tsaro da kasar ke fuskanta.

Buratai ya ce, an kafa rundunar sojin ne bayan lura da girman matsalar barazanar tsaro dake damun jahar da ma illahirin yankunan shiyyar arewa maso yammacin Najeriyar.

Ya ce tuni majalisar gudanarwar sojojin kasar ta amince da kafa wannan runduna karkashin dokar yaki ta 2016.

Jami'in sojin yace kafa wannan runduna yana daga cikin dabarun da za su taimaka wajen tunkarar kalubalolin tsaro dake addabar kasar.

Ya ce musamman, jahar na fama da matsalolin barayin shanu, da 'yan fashi da makami da masu dauke da makamai, da masu aikata muggan laifuka a kan iyakokin jahar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China