in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Faransa da Jamus a shirye suke su yi aiki da Rasha don tabbatar da shirin tsakaita bude wuta a Syria
2018-02-26 09:58:23 cri
Jiya Lahadi kasashen Faransa da Jamus suka bayyana aniyarsu na yin aiki tare da kasar Rasha da sauran takwarorinsu na nahiyar Turai don tabbatar da shirin tsakaita bude wuta tsakanin bangarorin dake yaki da juna a Syria, wanda hakan zai baiwa kasashen duniya damar yin aiki tare wajen amfani da matakan siyasa don warware rikicin kasar karkashin yarjejeniyar nan ta birnin Geneva.

Wannan ya biyo bayan wata sanarwar hadin gwiwa ne wanda shugaban Faransa Emmanuel Macron da shugabar gwamnatin Jamus Angel Merkel suka fitar, bayan wata tattaunawar da suka yi ta wayar tarho tsakaninsu da shugaban kasar Rasha Vladimir Putin.

Macron da Merkel, sun bukaci Rashar da ta matsawa gwamnatin Syriar lamba don ganin ta dakatar da kaddamar da hare-haren boma bomai kan 'yan tawaye ba tare da bata lokaci ba, kana ta hanzarta aiwatar da yarjejeniyar da kwamitin sulhun MDD ya amince da shi a ranar Asabar, tare da aiwatar da kyakkyawan tsarin sanya ido kan yarjejeniyar, kamar yadda fadar shugaban kasar Faransa ta sanar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China