in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Kenya ya taya jama'ar kasar Sin murnar sabuwar shekara bisa kalandar gargarjiya ta kasar Sin
2018-02-15 13:16:48 cri
A ranar 14 ga wata, shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta ya gabatar da jawabin taya murnar sabuwar shekara bisa kalandar gargajiya ta kasar Sin. A cikin jawabinsa, ya bayyana cewa, shi da jama'ar kasar Kenya suna taya jama'ar kasar Sin murnar zuwan sabuwar shekara.

Kenyatta ya bayyana cewa, Sin da Kenya sun sada zumunta a dogon lokaci. A cikin shekaru fiye da 600 da suka gabata, kasashen biyu sun samu nasarori na hadin gwiwa. Ya ce ya yi imani da cewa, za a raya dangantakar dake tsakanin Sin da Kenya zuwa wani sabon matsayi a nan gaba.

Kenyatta ya bayyana cewa, Sin da Kenya sun yi hadin gwiwa wajen kafa hanyoyin jiragen kasa a tsakanin Mombasa da Nairobi da sauran manyan ayyuka, wadanda suke kyautata zaman rayuwar jama'ar Kenya. Shugaban ya ce hanyoyin jiragen kasa a tsakanin Mombasa da Nairobi aiki ne mafi girma na more rayuwa a gabashi da tsakiyar nahiyar Afirka, kana alama ce ta shaida hadin gwiwa da sada zumunta a tsakanin kasashen Sin da Kenya da jama'arsu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China