in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kenya na da kyakkyawan fatan samun karin jarin waje
2018-02-08 10:34:00 cri
Babban manajan daraktan hukumar zuba jari ta kasar Kenya Moses Ikiara, ya ce kasar na samun karin masu sha'awar zuba jari a wannan shekara ta bana.

Mr. Ikiara ya ce ko da yake da yawa daga masu zuba jari sun rika dari darin zuba kudaden su a cikin kasar, sakamakon dambarwar siyasar da aka fuskanta a bara, amma yanzu komai ya daidaita, kuma tuni an fara gudanar da hada hada bisa damar da kasar ke samarwa.

Jami'in wanda ya bayyana hakan a jiya Laraba, yayin zantawar sa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua, ya ce Kenya na da damammaki na zuba jari masu yawa, kuma gwamnati na da kyakkyawan fatan cin gajiya mai tarin yawa daga kudaden da za a zuba a matsayin jarin waje a cikin kasa.

Mr. Ikiara ya buga misali da kamfanin "Nippo Express" da babban ginin Pinnacle da aka kaddamar ba da dadewa ba, a matsayin alamu dake nuna fara hada hadar zuba jari a kasar. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China