in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 2 sun mutu a sakamakon harin bom da aka kai a kan iyakar kasar Kenya
2018-01-29 10:44:27 cri
Jami'i mai kula da yankin arewa maso gabashin kasar Kenya Mohamed Saleh ya bayyana a jiya Lahadi cewa, an kai wani harin bam da aka dana a gefen titi a birnin Garissa dake arewa maso gabashin kasar dake dab da kan iyaka da kasar Somaliya, harin da ya haddasa mutuwar sojoji a kalla 2 tare da raunata mutane da dama.

Jami'in ya bayyana wa 'yan jarida cewa, motar dake dauke da sojojin ta taka nakiyar da aka binne a gefen titi ne. Rundunar 'yan sandan yankin tana zaton dakarun kungiyar Al-Shabaab ne suka binne nakiyar. An dai riga an tura wani rukunin sojoji zuwa wurin da lamarin ya faru don ganin an kama maharan

Salah ya kara da cewa, an kai gawawwakin sojojin da suka mutu a sakamakon harin da ma sojoji da suka ji rauni zuwa asibitin dake birnin Nairobi domin yi musu magani. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China