in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin na fatan kasashen duniya za su tinkari ta'addanci bisa tunanin bunkasa al'umma mai kyakkyawar makoma
2018-02-14 19:19:29 cri
A ranar Talata 13 ga watan nan, zaunannen wakilin kasar Sin dake MDD Mr. Ma Zhaoxu, ya gabatar da jawabi a gun taron kwamitin sulhun MDD, inda ya yi kira ga gamayyar kasa da kasa, da su kafa tunanin bunkasa al'umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil'adama, matakin da zai kara bunkasa hadin gwiwa wajen yakar ta'addanci, bisa sabon halin da ake ciki yanzu.

Mr. Ma ya kara da cewa, a lokacin da ake fuskantar barazana iri iri da ayyukan ta'addanci ke haddasawa, ya kamata kasashen duniya su bi ma'auni iri daya, su kuma sa niyyar yakar ta'addanci ba tare da nuna sassauci, ko ma'aunai mabanbanta kan yaki da ta'addanci ba.

Bugu da kari, a lokacin da ake kokarin tinkarar ta'addanci, ya kamata a mutunta ikon mulkin kasar da abun ya shafa. Sannan ya kamata kowace kasa mai alaka ta sauke nauyin dake wuyanta, ta yi kokari matuka wajen yakar ta'addanci.

Kaza lika Mr. Ma ya ce, ya kamata a bi ruhi da ka'idojin kundin mulkin MDD, a taka rawar MDD da kwamitin sulhun MDD wajen tinkarar ta'addanci cikin hadin gwiwa.

A matsayin wata muhimmiyar mamba daga cikin kasashen dake kokarin yakar ta'addanci. A 'yan shekarun baya bayan nan, kasar Sin ta kara yin hadin gwiwa da MDD da kungiyar hada kai ta Shanghai wato SCO, ta bayar da muhimmiyar gudummawarta wajen tinkarar ta'addanci tsakanin kasa da kasa. Don haka kasar Sin tana son ci gaba da hada kan sauran kasashen duniya, wajen shawo kan barazanar ta'addanci, da kuma shimfida zaman lafiya da kwanciyar hankali a duk fadin duniya. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China