in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Daliban Najeriya 22 sun hallaka a hadarin mota
2018-02-14 10:49:38 cri

Wasu dalibai 22 da direban mota sun mutu a yayin da motar da suke ciki ta yi taho mu gama da wata babbar mota a lokacin da suka kan hanyarsu daga jihar Bauchi zuwa Kano a arewacin Najeriya, wani jami'i ya tabbatar da faruwar lamarin jiya Talata.

A cewar Kabir Ibrahim-Daura, kakakin hukumar kiyaye hadarurruka ta jihar Kano, akwai wasu mutane uku da suka samu munanan raunuka a lokacin hadarin.

Ya ce daga cikin daliban 22, guda 12 maza ne, sannan 10 mata ne.

Najeriya tana daga cikin kasashen duniya da aka fi samun yawaitar hasarar rayuka a sanadiyyar hadarurrukan mota, galibi an fi samun matsalar ne sakamakon rashin kiyaye dokokin tuki, da rashin kyawun titunan mota ko kuma na ababen hawan.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China