in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mai yiwuwa yawan mutanen da suka mutu a hadarin jirgin ruwan Bahar Rum zai haura 200
2016-11-04 10:30:55 cri
Hukumar kula da bakin haure ta duniya, wadda hedkwatarta ke Geneva na kasar Swiss ta ce, kifewar jiragen ruwa sau biyu da suka abku a tekun Bahar Rum, mai yiwuwa ne adadin mutanen da suka hallaka zai zarta 200.

Hukumar ta bayyana hakan ne a yayin ganawa da manema labaru, tana mai cewa, a ranar 2 ga wannan wata, wani jirgin ruwa mai dauke da mutane fiye da 140 da ya nufi ratsa Bahar Rum zuwa Turai ya kife, inda mutane 27 kawai aka ceto bayan hadarin. Baya ga haka, wani jirnin ruwa na daban mai dauke da mutane kimanin 130 shi ma ya kife jim kadan bayan da ya bar gabar tekun Libya, an ce mutane 2 ne kadai aka ceto da ransu.

Bisa kididdigar da hukumar ta yi a cikin wannan shekarar, yawan bakin haure da 'yan gudun hijira da suka rasa rayukansu sakamakon hadarin jiragen ruwa a Bahar Rum ya wuce 4200, wanda ya zarta na shekarar da ta gabata wato 3770. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China