in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Adadin wadanda suka rasu sakamakon rubtawar gini a Uyo ya karu
2016-12-12 09:40:59 cri
Rahotannin baya bayan nan na cewa adadin mutanen da suka rasu sakamakon faduwar ginin cocin nan ta birnin Uyo a jihar Akwa Ibom dake tarayyar Najeriya ya karu zuwa sama da mutum 100.

Yanzu haka dai hukumomi na ci gaba da tattara alkaluman wadanda hadarin ya rutsa da su.

Wani jami'in lafiya a birnin ya bayyanawa majiyar mu cewa, an garzaya da wasu daga majinyatan zuwa asibitoci masu zaman kan su dake sassa daban daban na birnin Uyo. Kaza lika ya bayyana cewa 'yan sanda da sauran jami'an tsaro basu bayyana takamaiman adadin wadanda wannan lamari ya shafa ba.

A daya hannun kuma, wani jami'in rundunar 'yan sandan jihar ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, gwamnan jihar Udom Emmanuel na cikin wadanda suka tsira ba tare da samun wani rauni ba yayin da ginin ya fadi, sai dai kuma jama'a da dama sun rasu baya ga wasu da suka jikkata.

Gwamnatin jihar Akwa Ibom dai ta ayyana Lahadi da Litinin din nan a matsayin ranekun zaman makoki, domin jimamin aukuwar wannan lamari. Har ila yau gwamna Udom Emmanuel ya bada umarnin cafke dan kwangilar dake ginin cocin da ta rubza, a wani mataki na tantance musabbabin aukuwar hadarin.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China