in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bangaren Sin na fatan kasashen Koriya ta arewa da Amurka za su fuskanci daukar mataki mai ma'ana ba tare da taba lokaci ba
2018-02-13 19:53:54 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Mr. Geng Shuang, ya bayyana a nan Beijing cewa, bangaren Sin na fatan kasashen Koriya ta arewa da Amurka za su yi amfani da damar da ake da ita a yanzu, su nuna sahihanci, ta yadda za su iya sa niyyar daukar matakai masu ma'ana ba tare da bata lokaci ba.

Mr. Geng Shuang ya fadi haka ne a lokacin da yake bayyana ra'ayinsa game da sabbin ra'ayoyin da bangarorin da abin ya shafa suka bayar, game da sabon halin da ake ciki a yankin Koriya.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, ma'aikatar kula da harkokin dinkuwar Koriya ta kudu ta bayyana cewa, a nan gaba, bangaren Koriya ta kudu za ta fi mai da hankali kan lallashin kasashen Koriya ta arewa da Amurka da su tattaunawa tsakaninsu.

A waje daya, mataimakin sakatare mai kula da harkokin wajen kasar Amurka Mr. Mike Pence, ya kuma bayyana cewa, kasashen Amurka da Koriya ta kudu sun cimma matsaya daya kan batun nukiliyar Koriya ta arewa, wato daga farko bangaren Koriya ta kudu zai soma yin mu'amala da tattaunawa da bangaren Koriya ta arewa, sannan mai yiyuwa ne kasashen Amurka da Koriya ta arewa za su yi mu'amala da tattaunawa tsakaninsu kai tsaye a nan gaba. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China