in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana fatan DPRK da ROK za su yi amfani da gasar Olympics ta lokacin sanyi ta 2018 wajen inganta alaka a tsakaninsu
2018-01-02 21:05:51 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya ce, kasar Sin tana goyon bayan kasashen Koriya ta Arewa da takwararar ta kudu za su yi amfani da gasar wasannin Oylmpics ta lokacin sanyi da kasar Koriya ta kudu za ta karbi bakunsa a watan Fabrairu, wajen kokarin inganta huldar dake tsakaninsu.

Rahotanni na cewa, a jiya ne shugaba Kim Jong Un na Koriya ta Arewa ya ce, a shirye kasarsa take ta tattauna da Koriya ta Kudu, game da yiwuwar kasar ta halartar gasar ta Olympics da za ta gudana a birnin PyeongChang na kasar Koriya ta Kudu a shekarar 2018.

Shi ma shugaba Moon Jae-in na Koriya ta Kudu ya yi maraba da jawabin da takwaransa na Koriya ta Arewa ya yi a murnar sabuwar shekara, inda ya umarci jami'an gwamnatinsa da su dawo tattaunawa tsakanin Koriyoyin biyu, kana su zana matakan da suka dace a dauka na ganin Koriya ta Arewar ta shiga gasar. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China