in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi maraba da bude kafar tattaunawa tsakanin Koriya ta arewa da takwararta ta kudu
2018-01-03 20:17:01 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya ce kasar Sin ta yi na'am da kudurin Koriya ta arewa da takwararta ta kudu, game da sake bude kafar tattaunawa da juna tsakanin sassan biyu.

A ranar Larabar nan ne dai Koriya ta Arewa ta bude kafar shiga zirin Panmunjom wanda ya dade a rufe. Ana sa ran wannan kafa za ta bada dama ga kasashen makwaftan juna, su zanta game da tawagar Koriya ta Arewa da ake fatan za ta halarci gasar wasannin lokacin hunturu da za a yi a birnin PyeongChang na Koriya ta kudu.

Makatin ya zo ne kwana guda, bayan da Koriya ta kudu ta bayyana shawarar gudanar da taron manyan jami'ai na kasa da kasa, domin tattauna batun samarwa tawagar jami'an damar zuwa Koriya ta kudu, taron da zai gudana a ranar 9 ga watan nan.

Game da hakan, Mr. Geng ya ce Sin na goyon bayan inganta dangantakar sassan biyu, da kaucewa ruwa wutar rikici, da raba zirin Koriya da makaman nukiliya. Har ila yau Sin na fatan sassan biyu za su yi amfani da wannan dama wajen cimma buri daya da zai amfane su. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China