in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a gudanar da taro kan kula da garuruwan Afrika a kasar Morocco
2017-11-28 09:43:18 cri
Mambobin kungiyar hadin kan birane da kananan hukumomi na Afrika UCLG Africa, sun yanke shawarar gudanar da taro a cikin watan Disamban 2018 a kasar Morocco.

Kamfanin dillancin labarai na MAP ya ruwaito cewa, an yanke shawarar ne yayin taron kwamitin zartaswar kungiyar da ya gudana ranar Asabar da ta gabata a garin Grand Bassam na kasar Cote d'Ivoire.

Shugaban kungiyar shugabannin kananan hukumomin Morocco Mohammed Boudra, ya ce za a gudanar da taron a Morocco ne la'akari da kokarinta na tabbatar da daidaito tsakanin birane da kuma yankuna.

An shirya gudanar da taron a Morocco ne bayan birnin Brazzaville na kasar Congo, ya janye daga karbar bakuncinsa, saboda matsalolin kudi da kasar ke fuskanta a halin yanzu.

UCLG Africa, kungiyace ta hadin kai da wakilan kananan hukumomin Afrika, wadda ta kunshi kungiyoyi 40 na kanana hukumomi na kasa daga dukkan sassan Afrika da kuma birane 2000 dake da mazauna sama da 100,000. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China