in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Adadin mutanen da suka kauracewa muhallansu ya karu a DRC a shekarar 2017
2018-02-10 13:25:30 cri
Mai magana da yawun MDD Farhan Haq ya sanar cewa, sama da mutane miliyan 2 ne rikici ya tilastawa ficewa daga gidajensu a jamhuriyar demokaradiyyar Kwango DRC a shekarar 2017, inda ya rubanya adadin mutanen da suka kauracewa gidajen nasu a shekarar 2016.

Bisa ga alkaluman, a mafi karanci iyalai kusan 50 ne rikicin ke tilasta musu kauracewa gidajensu a cikin ko wace sa'a guda a tsawon shekarar ta 2017, kamar yadda Farhan Haq, ya bayyana cikin rahoton da ofishin kula da al'amuran jin kai na MDDr ya fitar.

Haq ya ce, a halin yanzu yawan mutanen dake zaune a sansanonin 'yan gudun hijira a kasar ya tasamma miliyan 4 da dubu 49, kuma sama da kashi 60 bisa 100 na adadin mutanen kananan yara ne. Wannan shi ne adadi mafi yawa na mutanen da rikici ya tilasatawa ficewa daga mutsugunansu a Afirka baki daya.

A shekarar nan ta 2018, ana bukatar dala biliyan 1.68 don samar da agaji ga mutanen na DRC, amma har ya zuwa yanzu, kashi 3 bisa 100 kawai na kudaden da ake bukata aka tattara.

Rashin tsarin gwamnati mai inganci, da matsalolin hare haren kungiyoyi masu dauke da makamai, da yawaitar take hakkin bil Adama a kasar, kana da samun jinkirin wajen gudanar da manyan zabukan kasar sun haifar da matsanancin talauci a tsakanin al'ummar DRC.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China