in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyoyin kasa da kasa sun yi kira a aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma DRC
2017-02-17 10:32:36 cri
Wasu kungiyoyin kasa da kasa ciki har da MDD sun nuna damuwarsa kan yadda ake samun jinkiri wajen aiwatar da yarjejeniyar siyasar da aka cimma a jamhuriyar demokiradiyar Congo.

Wata sanarwar hadin gwiwa da kungiyar tarayyar Afirka, da MDD, da kungiyar tarayyar Turai(EU) da kuma kungiyar kasashen dake magana da harshen Faransanci(IOF) suka sanyawa hannu, sun bayyana cewa, makonni shida tun bayan amincewa da tanade-tanaden gwamnatin wucin gadi, wadda daga bisani za a gudanar da karbabben zabe a watan Disamban shekarar 2017, har yanzu bangarorin da abin ya shafa ba su kammala tattaunawa game da matakan aiwatar da wannan yarjejeniya ba. Kuma hakan na iya mayar da hannun agogo baya.

Kungiyoyin sun kuma yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki a kasar, ciki har da magoya bayan shugaban kasa da bangaren 'yan adawa da su kara himma, don ganin an kammala wannan tattaunawa.

Haka kuma.kungiyoyin sun bukaci dukkan bangarorin kasar, da su goyi bayan yunkurin shiga tsakanin da taron CENCO ke jagoranta, tare da tabbatar da ganin an aiwatar da yarjejeniyar ranar 31 ga watan Disambar da aka sanyawa hannu. Matakin da zai kai ga gudanar karbabben zabe a kasar.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China