in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Burundi ya nemi a karfafa hadin gwiwa tsakanin Sin da Burundi
2018-02-07 14:03:40 cri
Shugaba Pierre Nkurunziza na kasar Burundi ya bayyana cewa dangantakar dake tsakanin Sin da Burundin ta kasance dangantaka mafi karfi idan aka kwatanta dangantakar dake tsakanin kasarsa da sauran kasashen duniya.

Kana ya kuma yabawa kasar ta Sin, inda ya bayyana cewa kasar Sin amintacciyar kasa ce wanda za'a iya dogara da ita ta fuskar mu'amala.

Nkurunziza ya bayyana hakan ne a lokacin tattaunawa da kafafen yada labaran kasar Sin, ya ce babban abin da ya karfafa kyakkyawar dangantaka tsakanin Burundi da Sin shi ne, an gina hadin gwiwar kasashen biyu ne bisa mutunta juna, da girmama juna, da kuma cin moriyar juna.

A bisa wata kididdiga daga ofishin jakadancin kasar Sin a Burundin ta nuna cewa, jarin cinikayya tsakanin kasashen biyu ya kai dala miliyan 46 a shekarar 2015. Kasar Sin tana sayen kofee da ganyen shayi mai matukar yawa daga kasar Burundi, yayin da kasar Sin ke sayar da kayayyakin sadarwa, da tufafi, da na'ura mai kwakwalwa zuwa kasar ta Burundi. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China