in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Satar bayanai da wasu kasashen yammacin duniya suka zargi kasar Sin ta yi wa AU karya ce, in ji shugaban Burundi
2018-02-07 13:19:34 cri
Kwanan baya ne, gabannin taron kolin kungiyar tarayyar Afirka wato AU karo na talatin, wata kafar watsa labaran kasar Faransa ta ruwaito wasu rahotannin dake cewa, wai kasar Sin tana satar bayanai a asirce game da harkokin AU. Shugaban kasar Burundi Pierre Nkurunziza ya bayyana cewa, gaskiya wadannan rahotanni ba su da tushe balle makama, kana, hanya ce kawai da wasu kasashen yammacin duniya suke amfani da ita domin gurgunta alakar dake tsakanin Sin da kasashen Afirka.

Yayin da yake zantawa da 'yan jaridun kasar Sin, Nkurunziza yana mai cewa, akwai wasu kafofin watsa labaran kasashen yammacin duniya wadanda ke amfani da rahotanninsu domin kawo cikas tsakanin wasu kasashe, da tunzura fitina ko haddasa kiyayya tsakanin kasashen duniya. Nkurunziza ya ce, wadannan kafofin watsa labarai ba za su cimma nasara ba, saboda yanzu kasar Sin babbar aminiyar hadin-gwiwar kasashen Afirka ne wadda ba za'a iya maye gurbinta ba.

Har wa yau, a madadin kasarsa wato Burundi, Nkurunziza ya godewa gwamnatin kasar Sin matuka saboda ta dade tana kokarin ganin an yi mata adalci a fadin duniya. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China