Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen Amurka, Heather Nauert ya ce, Amurka ta nuna damuwa sosai game da rikice-rikice a Sudan ta Kudu, inda ya ce, ma'aikatarsa zata zartas da wasu gyare-gyare kan manufofin kasuwanci kan Sudan ta Kudu, da takaita fitar da makamai da sauran wasu kayayyaki zuwa ga bangarori daban-daban da suke rikici da juna. Heather Nauert ya kuma yi kira ga kwamitin tsaron Majalisar Dinkin Duniya da ya azawa Sudan ta Kudu takunkumin hana jigilar makamai zuwa kasar.(Murtala Zhang)