in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An shawarci bangarorin da basa jituwa da juna a Sudan ta kudu da su kai zuciya nesa
2017-12-22 10:29:16 cri
Ma'aikatar harkokin wajen kasar Habasha ta shawarci bangarori biyu na kasar Sudan ta kudu da basa ga maciji da juna da su yi amfani da taron dandalin sulhutar rikicin kasar na (HLRF) dake gudana a hakin yanzu a matsayin muhimmiyar dama ta kawo karshen tashin hankalin dake damun jama'ar kasar.

Meles Alem, kakakin ma'aikatar harkokin wajen Habasha, ya bayyana a lokacin zantawa da manema labarai cewa, ana sa ran bangarorin Sudan ta kudun za su cimma matsaya wajen warware tashin hankalin dake addabar kasar ta hanyar amfani da dandalin na HLRF.

A taron da aka gudanar na majalisar ministocin kasashen gabashin Afrika IGAD karo na 59, an amince za'a mayar da hankali wajen amfani da taron dandalin na HLRF don tabbatar da yarjejeniyar tsakaita bude wuta da kuma samar da jin kai ga al'ummar dake bukatar agaji.

Alem, ya jaddada cewa al'ummar kasa da kasa za su dauki dukkan matakan da suka dace idan wannan tattaunawar ta ci tura don ganin an kawo karshen zaman tankiya a tsakanin bangarorin na Sudan ta kudu.

Firaiministan kasar Habasha kuma shugaba kungiyar IGAD na yanzu, Hailemariam Desalegn, ya bayyana a lokacin bude taron cewa, akwai bukatar bangarorin biyu na Sudan ta kudu da ba sa ga maciji da juna su kawar da banbance banbancen dake tsakaninsu.

A cewarsa, IGAD za ta dauki dukkan matakan da suka dace idan wannan tattaunawa ta faskara.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China