in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ofishin jakadancin Sin dake Zimbabwe ya shirya liyafar murnar bikin bazara
2018-02-03 14:03:44 cri
Jiya Jumma'a, ofishin jakadancin kasar Sin dake kasar Zimbabwe ya shirya liyafar murnar bikin bazara na kasar, wato biki mafi kasaita na al'ummar Sinawa. Ministan harkokin motsa jiki na Zimbabwe, da sauran wasu muhimman jami'an gwamnatin Zimbabwe gami da jakadun kasashen waje dake kasar, da wakilan kamfanonin kasar Sin dake Zimbabwe, da Sinawa dake wurin sama da dari shida ne suka halarci liyafar, inda suka yi murnar shiga sabuwar shekara bisa kalandar gargajiya ta kasar Sin wato shekara ta kare.

Jakadan kasar Sin dake Zimbabwe Huang Ping, ya taya mahalarta bakin murnar shiga sabuwar shekarar gargajiyar kasar Sin, da yi musu bayani kan al'adun gargajiya da suka jibinci wannan gagarumin biki wato bikin bazara. Huang ya ce, shekarar da ta shude, shekara ce dake da matukar muhimmanci ga Sin da Zimbabwe. Jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin ta yi nasarar kira babban taron wakilanta karo na 19 a Beijing, kuma tsarin gurguzu mai sigar musamman ta kasar Sin ya shiga sabon yanayi. Ita ma Zimbabwe ta zabi sabon shugabanta. Jakadan Huang ya ce, bayan da Mnangagwa ya hau karagar mulkin kasar, gwamnatin kasar Sin ta tura wakilinta na musamman zuwa kasar ba tare da wani jinkiri ba, lamarin da ya shaida irin kudirin gwamnatin kasar Sin na karfafa hadin-gwiwa da raya dangantaka tare da Zimbabwe.

Mista Huang ya kara da cewa, a shekara ta 2018, za'a iya samun kyakkyawar makoma wajen raya huldodin Sin da Zimbabwe. Shugaban Zimbabwe Mnangagwa zai ziyarci kasar Sin a watan Afrilu, kana kuma za'a kira babban taron dandalin tattaunawa kan hadin-gwiwar Sin da Afirka wato taron FOCAC a watan Satumba a Beijing. Babu tantama hadin-gwiwar Sin da Zimbabwe zata kara samar da alfanu ga al'ummar kasashen biyu.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China