in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Zimbabwe ya bukaci 'yan kasarsa dake ketare su koma gida
2017-12-22 10:03:01 cri
Shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa ya bukaci 'yan kasar dake zaune a kasashen ketare da su koma kasarsu biyowa bayan yin murabus din da tsohon shugaban kasar Robert Mugabe ya yi daga shugabancin kasar.

Mnangagwa, wanda a halin yanzu yake ziyarar aikinsa ta farko a kasar Afrika ta kudu, kuma ita ce ziyararsa ta farko zuwa kasashen ketare tun bayan da ya dare kujerar shugabancin kasar ta Zimbabwe a ranar 24 ga watan Nuwambar 2017

Da yake jawabi a gaban dandazon 'yan kasar Zimbabwean a Pretoria na kasar Afrika ta kudu, Mnangagwa ya ce, lokaci ya yi ga 'yan kasar dake zaune a kasashen waje za su koma gida.

Miliyoyin 'yan kasar Zimbabwe ne suka tsere zuwa kasashen waje, mafi yawansu sun kaura ne zuwa kasar Afrika ta kudu a tsawon lokacin mulki mista Mugabe na shekaru 37.

Mnangagwa ya ce 'yan kasar Zimbabwean dake zaune a Afrika ta kudu ya kamata su koma gida, kana su yi amfani da irin kwarewar da suka samu a makwabciyar kasar don sake gina tattalin arzikin kasar ta Zimbabwean da kuma gina cigaban kasarsu ta asali.

Tun a ranar Alhamis ne, Mnangagwa ya gana da shugaba Zuma, kuma dukkannin shugabannin biyu sun sha alwashin yin hadin gwiwa don gina tattalin arziki da cinikayya a tsakanin kasashen biyu.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China