in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta goyi bayan MDD wajen ba da karin gudummawa kan kiyaye zaman lafiyar duniya
2018-02-01 11:04:37 cri
Sabon zaunannen wakilin kasar Sin dake MDD Ma Zhaoxu ya bayyana a jiya cewa, kasar Sin za ta hada kai da sauran kasashen duniya don ganin MDD ta kara taka rawa a kokarin da ake na tabbatar da zaman lafiya a duniya, da kuma ciyar da bunkasuwar kasashen duniya gaba.

A ganawarsa da manema labarai bayan ya gabatar da takardarsa ta kama aiki a matsayin wakilin kasar Sin a MDD ga babban magatakardan MDD, Ma Zhaoxu ya bayyana cewa, kasar Sin za ta ba da gudummawa na kashin kanta a kokarin da ake na kafa sabuwar dangantakar kasa da kasa ta hanyar girmama juna, nuna adalci da cin moriyar juna, da gina al'umma mai kyakkyawar makoma.

Ya kara da cewa, a matsayinta na zaunanniyar mamba a kwamitin sulhu na MDD, kasar Sin za ta dukufa wajen kare matsayi da kuma martabar MDD yadda ya kamata, za kuma ta goyi bayan rawar da MDD take takawa. Haka kuma, ya ce, kasar Sin za ta sauke nauyin dake kanta na kasa na kasa sannan za ta shiga a dama da ita a kokarin da ake na tafiyar da harkokin kasa da kasa gyaran fuska. Haka kuma zai ci gaba da baiwa manufofi da shirye-shiryen kasar Sin goyon baya, kuma kasar Sin za ta ci gaba da zama mai kokarin tabbatar da lafiya da ci gaban duniya da kuma kiyaye dokokin kasa da kasa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China