in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Libya sun kashe wasu mayakan IS a kudancin kasar
2018-02-01 10:06:53 cri
Rundunar sojan kasar Libya ta bayyana cewa, dakarunta sun yi nasarar kashe wasu mayakan IS biyu a birnin Brak Al-Shati dake kudancin kasar.

Wani sojan dake aiki a runduna ta 12 ta sojojin kasar Mohamed Magrahi ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua a jiya Laraba cewa, an kashe mayakan na IS guda biyu ne a wani bata kashi tsakanin mayakan da sojojin rundunar da kuma mazauna birnin. Sojojin dai sun tunkari wasu mutane uku ne da suka zo sayan kaya a wani shago dake yankin domin su bayyana kansu, amma daga bisani sai suka fara nuna shakku a kan mutanen, daga nan ne mutanen da ake zargi suka harbe wani soja har lahira kafin daga bisani su gudu da motarsu.

Magrahi ya ce, ana haka ne kuma sai wani soja da wasu matasan birnin suka budewa mutanen da ake zargin 'yan ta'adda ne wuta, inda suka fafare su har zuwa inda motarsa ta lalace. Daga bisani an samu biyu daga cikin mutanen a mace a wajen birnin.

Mayakan IS dai na yawan kai koma tsakanin wajen birnin dake kudancin kasar, inda suke amfani da yanayin hamadar da ta tsara yankin suna kaddamar da munanan ayyuka. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China