in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Fashewar motoci masu dauke da boma-bomai a Libya ta kashe a kalla wasu 22
2018-01-24 13:39:11 cri
A jiya Talata an kaddamar da tagwayen hare-haren boma-bomai cikin wasu motoci a garin Benghazi dake gabashin kasar Libya, lamarin da ya haddasa rasa rayukan a kalla mutane 22, in ji wani asibitin yankin.

Kamfanin dillancin labarai na kasar Libya ya ruwaito cewa, mota ta farko ta fashe a gaban wani masallaci dake unguwar Salmani ta garin Benghazi, a lokacin da mutane da yawa suke addu'a a cikin masallacin. Sa'an nan, bayan da motar asibiti ta isa wuri don ceton wadanda suka jikkata, mota ta 2 ta kara fashewa, lamarin da ya haddasa rasa rayukan karin mutane masu yawa.

A cewar Fadia Al-Barghathi, kakakin asibitin Al-Jalaa na garin Benghazi, a kalla wasu mutane 22 sun rasa rayukansu, yayin da sauran 21 suka jikkata. Sai dai jimillar ba ta shafi mutanen da aka garzaya da su sauran asibitoci ba.

Hare-haren wannan karo sun kasance mafiya muni cikin watannin da suka gabata. Zuwa yanzu babu mutum ko wata kungiya da ta fito fili ta dauki alhakin kaddamar hare-haren.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China