in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AMISON za ta horas da jami'an tsaron kasar Somaliya
2018-01-29 15:16:35 cri
Tawagar dake aikin wanzar da zaman lafiya a kasar Somaliya (AMISON) ta bayyana cewa, sabuwar tawagar jami'an 'yan sandan kasa da kasa da aka tura kasar Somaliya za ta sanya ido tare da horas da 'yan sandan kasar dabarun kula da doka da oda, yayin da kasar ke kokarin sake farfado da hukumominta na tsaro.

Babban jami'in tawagar AMISON REX Dundun wanda ya sanar da hakan a jiya Lahadi, ya ce, za a tura jami'an 'yan sanda 40 daga kasashen Ghana, da Kenya, da Najeriya da Saliyo da Uganda da Zambia da suka kammala horon sanin makamar aiki zuwa ofisoshin 'yan sanda daban-daban dake Mogadishu, babban birnin Somaliya da kuma jihohin dake inuwar kungiyar AMISON.

A don haka jami'an tawagar 'yan sandan na AMISON, ya yi kira ga jami'an 'yan sandan da su gudanar da ayyukansu kamar yadda dokokin tawagar suka zayyana. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China