in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi kira da a taimakawa 'yan Somaliya da bala'in fari ya galabaita
2018-01-18 11:07:23 cri
A jiya Laraba ne, jami'in kula da harkokin jin kai na MDD dake kasar Somaliya Peter de Clercq ya bayar da wata sanarwa, inda ya kira ga gamayyar kasa da kasa da su taimakawa 'yan kasar Somaliya kimanin miliyan 5.4 da ke fama da bala'in fari da kudin da ya kai dala biliyan 1.6

Sanarwar ta yi nuni da cewa, kanfan ruwan sama a lokacin damina ne ya sanya kasar ta Somaliya fadawa matsalar yunwa, lamarin da ya kara haifar da babbar barazana ga aikin samar da abinci a kasar. A hasashen da aka yi, 'yan kasar kimanin miliyan biyu da dubu 444 ke fuskantar matsalar rashin abinci, a yayin da wasu dubu 866 ke matukar bukatar taimakon abinci. Yawan mutanen da ke fama da yunwa a kasar ya karu da sau 10, bisa na shekarar bara

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, duk da cewa an dauki matakan yaki da bala'in yunwa a bara a kasar, amma jan aiki wajen kawar da matsalar kwata kwata daga kasar. Sanarwar ta kuma yi kira da a taimaka wajen inganta kwarewar kasar Somaliya ta fannin tinkarar yunwa a yayin da ake samar mata da taimakon jin kai. (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China