in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta kara binciken shirin zuba jari ga waje da ya wuce dallar Amurka miliyan dari 3
2018-01-29 13:21:25 cri
Kwanan baya, ma'aikatar kasuwanci ta kasar Sin da wasu ma'aikatun kasar guda 7 suka fidda wani sabon tsarin zuba jari a kasashen waje, inda suka nuna cewa, daga yanzu za su rika gudanar da bincike kan duk jarin da ya kai ko kuma ya wuce dallar Amurka miliyan dari 3 da ake shirin zuba wa a kasashen waje, jarin da ake shirin zubawa a yankuna da ayyukan musamman, hasarar kudade masu dimbin yawa da aka yi sanadiyar zuba jarin waje da dai sauransu.

Jami'in harkokin kasuwanci a sashin hadin gwiwa a ma'aikatar harkokin kasuwancin kasar Sin Han Yong ya yi bayani cewa, a wannan karo, an bullo da ka'idojin sa ido kan harkokin zuba jari a kasashen waje, wadanda suka hada da gudanar da binciken shirin da kuma fanninsa, tattara bayanan shirye-shirye tare, da kuma hukunta wadanda suka sabawa ka'idoji.

Haka kuma, ana gudanar da bincike kan dukkan harkokin zuba jari, da suka hada da sha'anin kudi da wanda bai shafi sha'anin kudi ba.

Alkaluman kididdigar na nuna cewa a shekarar 2017, yawan kasashe da yankuna da kasar Sin take zuba jari kai tsaye ya kai 174, inda aka zuba jari dallar Amurka biliyan 120.08, adadin da ya ragu da kashi 29.4 bisa dari bisa na shekarar 2016. Kuma wannan shi ne karo na farko da adadin ya ragu tun daga shekarar 2003 da aka fara gabatar da shirin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China