in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na kan gaba a harkokin zuba jari a Afirka, a cewar wani rahoto
2017-06-29 09:10:20 cri
Wani rahoton da cibiyar bincike ta McKinsey ta fitar, ya nuna cewa harkokin raya tattalin arziki da kamfanonin kasar Sin ke gudanarwa a nahiyar Afirka, sun dara yadda aka tsammata a baya. Rahoton ya ce yanzu haka akwai kamfanonin kasar Sin da yawansu ya kai fiye da 10,000 dake hada hada a nahiyar.

Kaza lika rahoton ya bayyana cewa, bisa alkaluman kididdiga, kaso kusan 90 bisa dari na irin wadannan kamfanoni masu zaman kansu ne, kuma sun shafi fannoni daban daban, ciki hadda na samar da jari, da sabbin sana'o'i, da samar da jami'ai kwararru ga nahiyar.

A daya hannun rahoton ya bayyana sassa 5 da suka kunshi cinikayya, da zuba jari da samar da kayayyakin more rayuwa, da na ba da tallafi, a matsayin wadanda kasar ta Sin ta fi sauran kasashe tasiri a nahiyar ta Afirka.

Bugu da kari rahoton ya gano cewa, dangantaka tsakanin Sin da nahiyar Afirka ta kara bunkasa cikin shekaru 10 da suka gabata, inda harkokin cinikayya tsakanin sassan suke ci gaba, da kaso kusan 20 bisa dari a duk shekara, kana sashen zuba jari kai tsaye ke fadada, da kaso 40 bisa dari a kowace shekara.

Rahoton ya ma ce kudaden da 'yan kasuwa Sinawa ke shigarwa Afirka na iya haura hasashen da ake yi da kaso 15 bisa dari, idan aka hada da sauran sassa da ba a kididdige su ba. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China