A ranar 25 ga wata, wata motar bus wanda ta taso daga kasar Burkina Faso ta tarwatse a tsakiyar kasar Mali, sakamakon taka boma-bomai, lamarin da ya haddasa rasuwar mutane 26, yayin da wasu suka jikkata, cikin wadanda suka rasu har da wasu 'yan kasar Burkina Faso.
A sanarwar da kwamitin MDD ya fitar, ya nuna goyon baya ga gwamnatin kasar Mali wajen yaki da ta'addanci, haka kuma kwamitin ya jaddada muhimmancin kara karfin yaki da ta'addancin a yankunan kasar baki daya. (Maryam)