in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yi gargadi game da dawowar mayakan 'yan ta'adda zuwa Afrika daga Iraki da Syria
2017-12-18 09:24:08 cri
Kungiyar tarayyar Afrika AU, ta ce daya daga cikin manyan kalubalolin da kasashen Afrika ya dace su dauki matakan shawo kansu shi ne, batun komawar mayakan 'yan ta'adda zuwa Afrika bayan da aka yi galaba kansu a kasashen Iraki da Syria.

AU ta nuna fargabar ne a lokacin wani muhimmin taron da ta gudanar karo na 11 wanda cibiyar nazari game da ayyukan ta'addanci ta Afrika (ACSRT), ta shirya a ranar Lahadi a birnin Algiers na kasar Algeriya.

Kungiyar AU ta bayyana damuwa inda ta ce dawowar mayakan zuwa Afrika zai iya gurgunta yunkurin tabbatar da zaman lafiya da tsaron nahiyar, kasancewar mayakan za su iya kafa wasu sabbin kungiyoyin ta'addanci wadanda za su yi amfani da su wajen kaddamar da hare haren ta'addanci, ba kawai a yankunan dake fama da matsalar tsaro ba, har ma da yankunan da ba su taba fuskantar barazanar hare haren ta'addancin ba.

Kimanin mayakan Afrika dubu 6 ne suka shiga kungiyar IS mai fafutukar kafa daular musulunci a kasashen Iraki da Syria, wadanda ake tsammanin za su iya komawa gida bayan da aka yi galaba kan kungiyar ta IS. Smail Chergui, jami'in wanzar da zaman lafiya da tsaro na kungiyar AU, ya ruwaito wani rahoton MDD cewa, wajibi ne kasashen Afrika su hada kansu don su yi aiki tare don magance barazanar tsaron.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China