in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kawancen yaki da ta'addanci na kasashen musulmi ya gudanar da taron ministocin tsaron kasa karo na farko a Saudiyya
2017-11-27 10:47:38 cri
A jiya Lahadi ne, kawancen yaki da ta'addanci na kasashen musulmi da kasar Saudiyya ta kafa, ya gudanar da taron ministocin tsaron kasa na kasashe membobin kawancen karo na farko a birnin Riyadh, babban birnin kasar Saudiyya, inda suka cimma daidaito kan yin kokari tare, wajen yaki da ta'addanci a fannoni daban daban.

A sanarwar bayan taron da aka fitar, an bayyana cewa, ta'addanci ya kawo barazana, da kalubale ga zaman lafiya da tsaro a dukkan sassan duniya, kuma kasashen musulmi su ne ke kan gaba wajen fuskantar wannan matsala.

Sanarwar ta kara da cewa, kasashe mahalarta taron sun tsai da kudurin yin hadin gwiwa da juna, da yaki da ta'addanci a fannonin warware hakikanin tunanin ta'addanci, da yada tunanin addini mafi dacewa, da yankewa kungiyoyin ta'addanci hanyoyin samun kudaden shiga, da kaddamar da hare-haren soja da dai sauransu, ta yadda za a kai ga murkushe ta'addanci baki daya.

An kuma tsai da kudurin cewa, za a gudanar da taron ministocin tsaron kasa da kasa na wannan kawance a kowace shekara, ko kuma a duk lokacin da bukatar hakan ta bijiro. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China