in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana za ta gudanar da atisayen yaki da ta'addanci
2017-11-22 10:59:50 cri
Ma'aikatar tsaron Ghana ta ce kasar za ta gudanar da wani atisaye da ya kunshi hukumomi daban-daban domin tantance kwarewa da shirin kasar na tunkarar ayyukan ta'addanci.

Daraktan saashen yaki da ta'addanci na ma'aikatar, kuma kwamishinan 'yan sanda George Asiamah ne ya sanar da hakan, inda ya ce atisayen da za a fara ranar 25 ga wannan watan, zai kara karfafawa tare da yi wa jam'ai bitar kwarewarsu kan tunkarar hare-hare da shawo kansu.

Duk da cewa Ghana ba ta taba fuskantar hari ba, George Asiamah ya ce abubuwan dake faruwa a bayan-bayan nan a makwabtan kasashe na yankin da ma duniya baki daya, abun damuwa ne matuka, inda ya ce barazanar ta tilastawa Ghana daukar matakan tunkarar hare-haren ta'addanci.

Ya ce hukumomin tsaro sun fara shirin wayar da kan al'umma, da nufin ilmantar da su tare da shigar da hukumomin kai agaji cikin shirye-shiyen bitar inganta kwarewar aiki, ciki har da dabarun da suka zarce na tunkarar yaki da manyan makaman kare dangi, domin kasar ta zauna cikin shirin yaki da hare-haren ta'addanci. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China