in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka zata ci gaba da matsawa Rasha lamba
2018-01-27 13:27:09 cri
Jiya Jumma'a, ma'aikatar harkokin kudin kasar Amurka ta sanar da cewa, za ta kakabawa kamfanoni 9 da mutane 21 takunkumi, domin matsawa Rasha lamba yadda ya kamata, har sai Rashar ta aiwatar da alkawarinta cikin yarjejeniyar Minsk daga dukkan fannoni.

A wannan rana da dare, ma'aikatar harkokin wajen kasar Rasha ta fidda wata sanarwa cewa, babu shakka kasar Amurka tana da ikonta na katse huldar tattalin arzikin dake tsakaninta da kasar Rasha, amma kasar Rashar ita ma tana da nata ikon kan wannan fanni. Kuma takunkumin da kasar Amurkar ta kakabawa kasar Rasha ba zai yi wani tasiri ba ko kadan, sai dai ma ya haddasa hasara ga kamfanonin kasar Amurkan. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China