in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na maraba da bunkasar dangantaka tsakanin Amurka da Rasha
2017-04-14 19:11:10 cri

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya yi maraba da irin ci gaban da ake samu, a dangantakar dake wanzuwa tsakanin kasashen Amurka da Rasha. Mr. Geng ya bayyana hakan ne a Juma'ar nan, yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa.

Geng ya kara da cewa, kyakkyawar alaka tsakanin kasashe manya dake da kujerun dindindin a kwamitin tsaron MDD kamar Amurka da Rasha, zai taimaka wajen wanzar da tsaro da zaman lafiya a sassan duniya, tare da bada damar tinkarar kalubalen da kasashen duniya ke fuskanta.

A cikin makon nan ne dai sakataren harkokin wajen Amurka Rex Tillerson, ya kai ziyarar aiki kasar Rasha, inda sassan biyu suka bayyana ci gaba da ake samu, a dangantakar su cikin wadannan shekaru.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China