in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU za ta kaddamar da mizanin awon ci gaba da Afirka ke samu a fannin noma
2018-01-26 09:24:49 cri

Wata sanarwa daga kungiyar hadin kan Afirka ta AU, ta bayyana shirin kungiyar na fidda wani bayani, na awon nasarar da nahiyar ke samu a fannin ci gaban noma wanda aka yiwa lakabi da AATS.

Ana dai sa ran kaddamar da bayanin ne yayin taron shugabannin kungiyar na 30 dake tafe a ranar 28 ga watan nan da muke ciki. AATS zai zamo bayani irin sa na farko da kungiyar za ta gabatar, wanda zai kunshi sakamakon ci gaban noma da aka tattara daga sassan nahiyar daban daban.

Kaza lika kungiyar za ta fitar da rahoton ta na shekaru biyu biyu game da yadda ake aiwatar da yarjejeniyar Malabo ta watan Yunin shekarar 2014, game da ci gaban da najiyar ke samu a fannin dabarun gaggauta ci gaban ayyukan gona, da kyautata zamantakewa da rayuwar al'ummun nahiyar.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China