in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sama da shugabannin Afirka 40 da babban sakataren MDD ne za su halarci taron kolin AU
2018-01-24 20:23:29 cri
Ministan harkokin wajen kasar Habasha Workneh Gebeyehu ya bayyana cewa, sama da shugabannin kasashen Afirka 40 da kuma babban sakararen MDD Antonio Guterres ne ake sa ran za su halarci taron kolin kungiyar tarayyar Afirka (AU) karo na 30 a birnin Addis Ababan kasar Habasha.

Ministan wanda ya bayyana haka Larabar nan yayin taron manema labarai, ya ce ana sa ran shugabannin za su tattauna kan batutuwan siyasa da tsaro da ke damun kasashen Afirka da kuma gyaran fuskan da ake fatan yiwa kungiyar da aka kafa shekaru 54 da suka gabata.

Taken taron kungiyar na wannan karo wanda aka bude a ranar Litinin, shi ne "Yaki da cin hanci da rashawa: hanya mai dorewa ta farfado da nahiyar Afirka". A ranar 29 ga wannnan wata ne ake fatan kammala taron, wanda aka saba gudanarwa sau biyu a shekara.

Kungiyar AU dai ta ayyana shekarar 2018, a matsayin shekarar yaki da cin hanci da rashawa a Afirka. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China