in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude zaman PRC yayin taron kolin kungiyar AU karo na 30
2018-01-22 19:00:09 cri
A yau ne shugaban hukumar zartarwar kungiyar tarayyar Afirka (AU) Moussa Faki Mahamat ya sanar da bude zaman taron wakilan din-din-din na kungiyar tarayyar Afirka(PRC) karo na 35 a hukumance a hedkwatar kungiyar dake birnin Addis Ababan kasar Habasha. Taron wakilan na PRC yana zuwa ne karkashin taron kolin kungiyar karo na 30.

Taron ya kuma samu halartar jakadun kasashe 55 na mambobin kungiyar dake Addis Ababa da kuma manyan jami'an kungiyar da sauransu.

A cewar shugaban, taken taron kolin kungiyar na wannan karo, shi ne, "yaki da cin hanci da rashawa: hanya mai dorewa ta farfado da nahiyar Afirka". Ana kuma sa ran taron wakilan na PRC zai duba tare da tattauna batutuwan da suka shafi aikin gona, sufuri, kimiya da fasahar kere-kere, watsa labarai da harkokin sadarwa na zamani da kuma batutuwan da suka shafi dokoki da harkokin kudi. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China