in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta yaki masu aikata munanan laifuffuka
2018-01-24 21:05:56 cri
Kasar Sin za ta fara aiwatar da wani sabon shirin yaki da munanan laifuffuka a wani mataki na tabbatar da tsaron jama'a da gina kyakkyawan tubalin tafiyar da harkokin jam'iyya yadda ya kamata.

Wata takarda da kwamitin koli na JKS da majalisar gudanawar kasar suka fitar a Larabar nan, ta bayyana cewa, shirin zai mayar da hanlali kan masana'antu da wuraren da ba ta gari ke amfani da su wajen aikata munanan laifuffuka wadanda ke zama barazana ga tsaron jama'a.

Takardar ta ce, tsaron jama'a shi ne kashin bayan tabbatar da zaman lafiya da tsaro ta yadda gwamnati za ta samu goyon bayan jama'a a matakin yankunan karkara. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China