in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta lashi takobin fadada ilimin Sakandare
2017-04-07 09:46:15 cri
Ma'aikatar ilimi ta kasar Sin ta sanar da cewa, ya zuwa shekarar 2020, kasar za ta fadada ilimin sakandare a fadin kasar da kashi 90 cikin dari zuwa sama, daga kashi 87.5 cikin dari da ake da shi a shekarar 2016.

Babban jami'i a ma'aikatar Lyu Yugang ya shaidawa manema labarai a jiya Alhamis cewa, duk da karuwar adadin daliban sakandare a kasar, yankunan dake fuskantar koma baya a tsakiya da yammacin kasar na ci gaba da fama da karancin kayayyakin koyo da koyarwa, sannan ci gaban fannin ilimin sana'o'i na tafiyar hawainiya.

Lyu Yugang ya kara da cewa, akwai rashin daidaito tsakanin sauran fannonin ilimin sakandare da kuma ilimin sana'o'i a gabashin kasar.

A cewar wani jadawali da ma'aikatar ta fitar jiya, daga shekarar 2017 zuwa 2020, kasar za ta inganta ilimin sana'o'i a makarantun sakandare da samar da kayayyakin koyo da koyarwa da kuma kara yawan kudin da ake warewa bangaren.

Jami'in ya ce, za a kara yawan kayayyakin aiki a makarantun dake yankunan dake fuskantar koma baya tare da tabbatar da hakkin ilimi ga dalibai masu bukata ta musammam da 'ya'yan da suka fito daga gidaje masu karamin karfi da na ma'aikata masu kaura. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China